Waiwaye: Naɗin manyan hafsoshin tsaro, sanya dokar ta-ɓaci kan satar waya a Kano

 Tinubu ya naɗa sabbin hafsoshin tsaron Najeriya





A farkon makon da ya gabatan ne shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗa sabbin manyan hafsoshin tsaron Najeriya da kwamandojin fadar shugaban ƙasa.

Matakin na zuwa ne bayan sabon shugaban ya sanar da sallamar hafsoshin da ke jagorantar rundunonin tsaron ƙasar daga aiki nan take.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, ta bayyana Mallam Nuhu Ribaɗu a matsayin Mashawarcin shugaban ƙasa kan harkar tsaro wato 'National Security Adviser'.

Shugaban Najeriyar dai ya naɗa Manjo Janar C.G Musa a matsayin babban hafsan tsaro, bayan sallamar Laftanal Janar Lucky Irabor.

Karanta cikakken labarin a nan

Tafiyar Tinubu taron harkokin kuɗi na duniya a Faransa
a
ASALIN HOTON,DADDY OLUSEGUN
Bayan naɗin sabbin jagororin tsaron ne kuma, shugaban na Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya kama hanyar faransa domin halartar taron nazari tare da rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya ta hada-hadar kudi ta duniya da aka gudanar a birnin Paris.

Yarjejeniyar za ta kasance ta fifita ƙasashe masu rauni wajen bayar da tallafi da saka hannun jari sakamakon mummunar tasirin sauyin yanayi, da kuma sakamakon cutar korona.

An dai tsara shugaba Tinubu zai koma Najeriya ranar Asabar, to sai da maraicen ranar ta Asabar fadar shugaban ƙasar ta fitar da wata sanarwa da maraicen ranar Asabar cewa shugaban zai zarce Birtaniya domin wata ziyara ta radin kansa.


Post a Comment

Previous Post Next Post